Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya halitta mutane, namiji da mace, kuma ya sanya su qabila-qabila domin su san juna. Tsira da aminci su tabbata ga manzonsa Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallama), wanda yake cewa “Kuyi aure ku hayayyafa domin nayi alfahari daku ranar alqiyama” da alayansa da Sahabbai da dukkan waxanda suka bishi har zuwa ranar sakamako.
Bayan haka yan’uwa na baiwa wannanyar qasida tawa taken gida mai cike da sa’adah domin zan bayyana waxansu haqqoqi dake kan miji da mata waxanda idan suka bisu zasu samu dacewa da rabauta duniya da lahira, kaucewa waxananan haqqoqi na iya sanya ruxani da rahsin jituwa tsakanin ma’aurata. Insha Allah zan fara da ambaton haqqoqi waxanda suka shafi haqqin miji akan matarsa;-
1. Yin biyayya matuqar babu savan Allah: Ya wajaba ga dukkan wata xiya mace wanda take neman yardar Allah tabi umarnin mijinta kowane lokaci, matuqar bai umurce ta da savon Allah ba, domin “Babu biyayya ga abokin halitta gurin savon Allah”. Kuma ta sani mijinta shi ne Aljannar ta ko wutar ta, kuma yardar miji mabuxi ne na samun Aljannah ga mata ta gari.
2. Kada ta yiwa wani umurni ya shiga gidansa face da izinin sa, savanin yadda gidajenmu suka zamar kamar kasuwa gurin shiga kowa da kowa.
3. Kada ta gujewa mijinta a duk lokacin da ya buqaci kwanciya da ita, a kowane lokaci sai dai lokacin da Allah ya hana a kwanta da ita wato lokacin da take al’adah.
4. Kada ta yi tasarrufi ko juya dukiyarsa ta kowane irin hali ba tare da izninsa ba, ko ta yi fachaka cikin dukiyarsa, domin Allah zai tambaye ta akan haka, domin yana daga cikin amana wanda Allah zai tambaye ta ranar Alqiyama, kasancewar ta mai kiwo ce a gidan mijinta. Saboda ya wajaba ta kasance mai lura mai kiyayewa.
5. Ba ya kamata gare ta ta juya dukiyar ta face da izninsa, saboda Hadisin Annabi dake cewa “Bai kama ga mata ta aikata wani abu daga dukiyar ta ba face da iznin mijinta”.
Koda tana aiki ne ko tana samu to ya kamata ta sani shi ne wanda ya yi mata iznin fita gurin wannan aikin, ko ma ya sadauqar da wani daga cikin haqqinsa, dana `ya’yansa, domin fitar ta gurin wannan aikin.
6. Ta kasance mai yi mashi hidima: Kamar yadda shi ma yake yi mata ta hanyar kula dashi da kula da gida da yaransa da dukan wasu xawainiya wanda ya shafi cikin gida.
7. Rashin yin jayayya dashi lokacin da ya yi fushi, ma’ana kada ta kasance mai musu ko jayayya dashi lokacin da ya yi fushi, domin hakan na iya jawosharri da samun matsala a wannan gida, mace mai hankali ita ce wacce take nisanta daga abin da zai sanya mijinta ya yi fushi, kuma ba ta jayayya dashi lokacin fushi.
8. Kada ta wuce iyaka gurin kishi: Musamman lokacin da za’a qaro ma ta abokiyar zama, domin duk lokacin da kishinta ya yi yawa yana iya haifar da watsewa da tarwatsewar gida.
9. Ta kasance cikin kyakkyawar kama a kowane lokaci, ma’ana a cikin gidanta tare da mijinta, ta hanyar yin shiga wacce yake so, da sanya kayan da yake so, da kasancewa cikin tsabta kowane lokaci, da kuma kula da makwancinsa, domin Annabi yana cewa “Mafi alkhairin mata ita ce wacce idan mijinta ya kalleta zai ji daxi, kuma tana yi mashi xa’a idan ya yi mata umurni, kuma ba ta sava masa akan da dukiyar ta da abin da baya so.
Ci gaba zai zo a bugu na gaba insha Allah.
UNDER MAINTENANCE
Allah ya saka da Alkyairi