An dade ana yada jita-jita akan Ahlus-Sunnah da cewa (wai) bamu yarda da samuwar waliyyai da karamominsu ba, kuma abin mamaki mutane da yawa suna gaskata wannan sharri da qage na zunzurutun qarya zuqalaqe (Zuqi ta mallo). Tare da cewar, a qa’idar shari’a ba a saurin gaskata jita-jita, domin mafi yawan ta shiryayyiyar qarya ce ko kuma banqara gaskiya, ana cakuxa ta da qarya don cimma wani mugun nufi. Sai dai kuma yayin da mutum ya leqa littattafan Sunnah, da kuma sauraron karatun malaman Sunnah, to, kai tsaye zai gano tantangaryar rashin adalcin masu faxin waccar Magana, kuma zai fahimci Aqidar Ahlus-sunnah dangane da waliyyi ko karamar waliyyai, sai dai abin da suke kaucewa shi ne xaukar waliyyai a matsayin mutanen da suka san gaibu, ko marasa savo, ko kuma yi musu biyayya ido rufe. Tare da basu matsayin da bai kaucewa ma’aunin shari’a ba, wato Qur’ani da Hadisi bisa fahimtar magabata nagari. Ya xan’uwa ka sani cewa, wannan rubutu bai isa warware maka duk abin da ya shige maka duhu ba, dangane da sha’anin waliyyi, face dai xan tsokaci ne akan: BAMBANCIN MU’UJIZA DA KARAMA. To amma ka sani cewa waliyyan gaskiya sune, duk mumini (mai imani na gaskiya) da kuma tsoron Allah, kenan duk wanda ka ganshi ko ka ji yana savawa tafarkin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam), ko yana umarni da haka, to, wallahi ba waliyyi bane, xan duniya ne, mai tallan vaqar haja. To, bari in fara da ma’anar mu’ujiza da ta karama. Na Farko: Mece ce Mu’ujiza? A taqaice dukkan abin da wani Annabi ko Manzo, zai yi na ban mamaki, da keta al’ada cikin yardar Allah, ana kiransa mu’ujiza. Kuma ta kevanci Annabawa ne ko Manzanni (Alaihimus Salam), kamar raya matacce ga Annabi Isah (A.S.), lamarin san da ga Annabi Musa, tsagewar wata, zancen damo, da sauransu ga Annabin mu Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam). Na biyu: Mece ce Karama? A shar’ance in ance karama, ita ce wani lamari da ya savawa al-ada, wanda Allah yake gudanar dashi a hannun wani mutumin kirki, mai cikakken imani da tsoron Allah, wanda shi ba Annabi ko Manzo bane, don taimakonsa kan wani lamari na Addini ko na duniya. Kuma Ahlussunnah sun yarda da karamar waliyyai bisa ma’aunin Qur’ani da Sunnah. Duba Aqidatul Wasixiyyah. To, amma kafin mu duba bambancin Mu’ujiza da karama, bari kaji! Da yawan mutane an xorasu akan cewa, mutum ba zai zama waliyyi ba, sai ya riqe wasu wuridai da zikirai, ya yi su, ya shiga abin da suke kira HALWA, wato ya guji duniya, ya qauracewa mutane, ya zama yana kwana da yunwa, yana yawo kamar mahaukaci, cikin datti, wasu kuma za su yi tsaftar, to, amma wai sai mutum yafita daga mutuntakarsa, ya zama yana da siffofi irin na… kamar yadda mai Jawahiril ma’ani yake cewa “Haqiqanin waliyyi shi ne wanda ya fita daga siffar mutuntaka gaba xaya, sannan ya yi ado da halayen Ubangijintaka, zahiri da baxini (wal’iyazubillah)” Duba Jawahiril Ma’ani 2//66. Wannan fa misalin waliyyi kenan, a wajen, masu cewa, wai bamu yarda da samuwar waliyyi ba, to, in har da irin wannan ake zama waliyyi a mahangarsu, to, ai sune ma suke qaryata waliyyan gaskiya masu imani da tsoron Allah, waxanda basa aikata wani aiki face, sai ya dace da koyarwar Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) babu daxi babu ragi. Na Uku: Bambancin Mu’ujiza Da Karama: Bari kaji malamin mu Malam Muhammad Rabi’u Umar R/Lemo, ya bambance mana tsakaninsu da faxinsa cewa “Karama tana da bambanci da mu’ujiza ta fuskoki da dama. Da farko dai ita kanta mu’ujiza, wato abin da Annabawa suke zuwa dashi, wanda ya savawa al’ada don tabbatar da Annabincinsa, ba ya zama gaskiya, ko ya nuna Annabcin wanda ya zo dashi, sai ta cika siffofi kamar haka: 1) Ya zama aikin da mai da’awar Annabta ya zo dashi, ba wanda zai iya yinsa sai Allah (Subhanahu Wata’ala). Da mutum zai yi da’awar Manzanci, ko ya ce shi Annabi ne, sannan ya ce mu’ujizarsa ita ce motsi da yake yi ko tsayuwa dayake yi ko zama ko tafiya, to ba ta zama mu’ujiza ba, saboda dukkan mutane ma zasu iya yin hakan. 2) Ta zama (mu’ujizar) ta savawa al’ada. Da mai da’awar Manzanci zai ce mu’ujiarsa ita ce, zuwan dare bayan rana, da hakan bai zama mu’ujiza ba. 3) Ya zama Mu’ujizar ta faru ne take lokacin da yake faxinta. 4) Kuma ta faru kamar yadda ya faxa, ba tare da ta savawa abin da ya faxa ba. Misali, da mai da’awar Annabci ko Manzanci zai ce, mu’ujizata ita ce, “Wannan dabbar ta yi magana” sai dabbar ta yi maganar, amma tace, “karya ka ke!” to, wannan ba mu’ujiza bace. Ci gaba zai zo a bugu na gaba insha Allah.
UNDER MAINTENANCE