– MAS’ALAH TA DAYA (1)
KIFI NA GANINKA ME JAR KOMA
RADDI GA SHEIKH ABDULJABBAR NASURU
KABARA (SHUGABAN ‘YAN KOWAYE!!!…)
MAS’ALAH TA DAYA.. (RUBUTU NA DAYA)
KHUDBATUL HAAJAH DA LAFAZIN “INNAL
HAMDA LILLAH …”
BISMILLAH, WASSALATU WASSALAMU ALA
RASULILLAH, WA ALA ALIHI WA SAHBIHI WAMAN
WAALAAH, BAYAN HAKA:
Kamar yadda bayani ya gabata cewa zamu dauki
wannan Raddi na Malam Muhammadul Kabeer da
yayiwa Abduljabbar, mu bishi daki-daki (tare da
taqaicewa) mu kawo shi a rubuce, to Insha Allahu
Yanzu zamu fara da Mas’alah ta daya daga
Mas’aloli biyar da Malam yayi bayani, wadanda
kuma aka musa su, kafin sannan ina me sanar da
mai karatu cewa:
1. A maimakon kawo Shafin Kowacce riwaya,
zan rika kawo Link (Maballin Likau), idan
kuma da dama zan hada duka biyun.
2. Idan na sami dama zan kawo mana
kowacce Mas’alah cikin sautinta, ma’ana
daga bakin Malam dan kara fito da ita fili.
3. Game da Lambar Hadeethi ko Athari da zan
kawo a link ba lalle bane ya zama daya da
na Malam, (saboda banbancin Mad’ba’ah).
4. Zan kawo links Gwargwadon iko, ban
shardanta kawo su gaba daya ba, (domin
hakan zai min wahala sosai).
5. Game da wani sharadi da na kafa na cewa
zamu duba kowacce mas’alah tare da Yan
uwa dalibai da kuma malamanmu, na janye
ta (sai dai duk wanda yaga gyara zai iya
gyarawa a comment box).
Wannan kenan, kafin mu shiga kai tsaye cikin
mas’alah ta farko zan kawowa mai karatu link da
zai sauke Raddi na Farko, domin saukewa shiga
nan:
Raddi Ga Abduljabbar (Na daya)
Malam Ya fara da kawo Riwayar da take tabbatar
da samuwar lafazin “Innal Hamda lillah…” wanda
Malam ya bayyana cewa wannan mas’alah ba
wata mas’ala bace da aka dauke ta da zafi, sai
dai yawan Musanta ta da ake yasa dole ayi
bayani.
1. Riwayar Abdullahi bn Mas’ud (R.a):
a. Imam Ibnu Abi-Shaibah , Ya kawo ta cikin
littafinsa ( Almusannaf , lamba ta 17798) ( a link
din da zan kawo za’a ga 17508 ne riwayar take,
wanda na riga nayi bayani a baya) daga [Humaid
bn Abdurrahman].
Domin duba wannan riwayar shiga nan:
Musannaf..
b. Imam At-tabaraniy, cikin littafin ( Addu’aa
lamba ta 933) ( a link din lamba ta 932 ne take )
daga [Adam bn Abi- Iyaas] .
Ga link din don karantawa:
Addu’aa
c. Alhaitham bn Kulaib wanda aka fi sani da
“shaashiy ” a cikin (Musnad nasa (Musnad lish
shaashiy) lamba ta 697).
( a link din lamba 652 ) daga [ Abdurrahman bn
ziyaad ].
Shiga nan ka karanta:
Shaashiy
Dukkanninsu
daga Mas’udiy daga Abi-Ishaq Assabee’iy daga
Abil-Ahwas – Awf bn Malik bn Najdah
Aljushamiy – daga Abdullahi bn Mas’ud (R.A)
Ya ce: …
alhadeeth.
“Saheehi ne a bisa sharadin muslim”.
2. Hadeethin Yana da Mutaaba’aat :
(Zan kawo su gaba dayansu tare da kawo kadan
daga cikin Links dinsu)
a. Imamut Tirmiziy , a cikin littafin ( Jami’ nasa
Hadeethi mai lamba ta 1105).
Shiga ka karanta:
Tirmizhiy
b. Imamun Nasaa’iy , a cikin littafinsa ( Assunanul
Kubraa, lamba ta 10249)
Shima zaka iya duba shi anan:
Annasaa’iy
c . Abu-awaanah , cikin ( Mustakhraj nasa, lamba
ta 3354) (a link kuma 3301).
Duba shi anan:
Abu Awanah
d. Ibnul-Jaarud a cikin littafin ( Almuntaqaa minas
sunanil Musnadah a lamba ta 679).
e. At-Tabaraaniy a cikin littafin ( Al-kabeer
‘Mu’jamul Kabeer’ 9934).
Dukkaninsu daga A’mash (Sulaiman bn Mihran)
f. Imamun Nasaa’iy a cikin littafinsa ( Sunanul
Kubra, lamba ta 10251)
shi kuma daga Zuhair (A’mash da Zuhair ) daga
Abi-Ishaq, daga Abil-Ahwas, daga Abdullahi bn
Mas’ud (r.a)… Da wannan lafazi dai na Innal
Hamda lillah…
“Dan haka a daina Kore Al’amura…!!!”
Zan dakata anan domin mai karatu yaji dadin
karatun, nima kuma na huta, domin kuma mai
bahasi ya sami damar bahasi.
Allah nake roko da Ya yassare min al’amura, Ya
bani ladan dai-dai din da ke ciki, Ya gafarta min
Kuskuren da ke ciki.
Allah Ya sakawa Malam Muhammadul-Kabeer da
Alkhairi, Ameen .
Wassalam… Mu hadu a rubutu na biyu.
Note :
Domin gyara, ko korafi, bada gudun mawa, ko
karin bayani, tambaya, ko neman karin bayani!!
… TAIMAKA KA RUBUTA A AKWATIN COMMENT